IQNA

'Yan Jarida 800 Ne Za Su Gudanar Da Aikinsu A Lokacin Aikin Hajjin Bana

23:43 - August 03, 2018
Lambar Labari: 3482857
Bangaren kasa da kasa, ma'aikatar kula da ayyukan hajji ta kasar Saudiyya ta ce 'yan jarida 800 za su gudanar da ayyukan bayar da rahotanni a lokacin aikin hajjin bana.

 

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, Awwad Bin Saleh ministan yada labarai na kasar saudiyya ya sanar da cewa, ma'aikatar kula da ayyukan hajji ta kasar Saudiyya ta ce 'yan jarida 800 ne daga ciki da kuma kasashen duniya za su gudanar da ayyukan bayar da rahotanni a lokacin aikin hajjin wannans hekara.

Y ace waddanan 'yan jarida za su mayar da hankali ne wajen gudfanar da ayyukansu tare da bayar da bayanai kan yadda aikin hajji yake gudana.

Haka nan kuma suna da damar da za su shiga wuraren da aka kayyade musu domin daukar rahoto a biranan Makka da Madina.

3735469

 

captcha